Sakon hajjin bana na
maigirma Ayatullahi sayyid Ali khamna,i,
shugaban juyin musulunci na jamhuriyar musulunci ta Iran
2006
Da sunan Allah mai rahma mai jinkai
Tsira da amincin Allah su tabbata ga manzon
Muhammad (S.A.W.A) da iyalansa tsarkaka. Da sahabbansa masu gaskiya.
Aikin hajji kamar kowace
shekare wanda ya cike da tarbiyyar ruhi
ya sake zagayowa wanda yake wata babbar damace ga duniyar musulunci. Duk da
cewa zukata daga sassa daban-danban suna cike da shaukin zuwa wannan wuri mai alfarma,
amma "yan kadan ne kawai suka
samu dacewa da zuwa wannan wuri mai
tsarki, sannan wannan yana daga cikin abin da ya kara wa wannan idanuwa mai
bubbuga albarka ta har abada.
Haduwar 'yan uwa musulmi daga ko'ina daga
sassan duniya acikin dakin masoyi, ta bangare guda wannan yana kara fuskantar
da al'umma zuwa ga mahalicci, ta bangare guda kuwa yana hada masoyan da suka nisanci junansu,
saboda haka wannan yana samar da nishadi na musamman tsakanin al'ummar musulmi.
Tsarkaka daga daudar zunubbai baki daya
acikin dukkan ayyuka a kowane wuri,
saduwa da ubangiji, duk da yake acikin 'yawanuka takaitattu, amma babban guzuri
ne ga dan Adam. Sakamkon ladubba da dukkan abinda ayyukan hajji suka kunsa duk
don mutum ya samu wannan ganawa da ubangijinsa ne wadda sakamakon haka zai
dandana wani zaki na musamman, sakamakon haduwarsa da ubangiji.
Ta bangaren siyasa kuwa, abu na farko da
aikin hajji yake nunawa shi ne hadin kai tsakanin al'ummar musulmi. Nisantar
al'ummar musulmi tsakanin juna shi ne yake janyo makiya su sanya ransu wajen
cin nasara akansu, sannan wanna ne yake taimakawa wajen kyankyasshe kwan sabani
a tsakanin al'ummar muslmi.
Al'ummar muslmi ta ginu ne daga mutane daga
kabiloli da harsuna daban-daban, sanann daga mazhabobi mabambanta. Wannan
bambance-bance wanda ya samu ta hanyar bambancin wurin zama ta yadda ya kasance
acikin wani yanki na musamman a bayan kasa. Wannan zai iya zama wani abu
ne wanda zai karfafa wannan al'umma ta
wata fuska. Sannan kayan tarihin da suka yi tarayya a tsakaninsu zai taimaka
wajen hada junasu, sannan su yi amfani da baiwar da suke da ita a matsayisu na
'yan Adam wajen tabbatar da gurinsu.
Yan mulkin mallaka tun farko sun kula da haka
shi ya sanya suka yi gaggawa wajen raba kan
al'ummar musulmi.
Shugabanni masu mulkin mallaka sun riga sun sani cewa, idan
duniyar muslmi ta kafu, to babu shakka mulkin mallakar da suke yi ta hanyar
tattalin arziki da siya zai kawo karshe. Saboda haka ne ta kowace hanya suke
kokarin suga sun kawo sabani acikin
al'ummar muslmi, a karkashin wannnan lemar ne suka yi amfani da jahilcin
mafi yawan al'ummar musulmi da shugabanni masu ko in-kula na siyasa da al'adu,
ta yadda suka samu damar mallakar kasashen musulmi ta hanyar siyasa da al'adu.
Dankwafar da kungiyoyi masu neman 'yanci a
tsawon karnin daya gabata a kasashen musulmi, sannan da gaggauta mallakar
kasashen musulmi ta hanyar masu mulkin mallaka, da samar da, ko karfafa
hukumomin kama karya na kasashen musulmi, da wawashe dukiyoyin wadannan
kasashe, da kawar da al'ummar wadannnan kasashe, da dankwafar da kasashen
musulmi ta yadda kada su cigaba ta fuskantar fasaha da kere-kere, wannan kuwa
duk karkashin inwar raba kan al'ummar muslmi ta yadda har yakan kai ga yakar
juna.
Amma bayan farkawar musulmi wanda ya kai kololuwarsa sakamakon samar da
jamhuriyar musulunci ta Iran,
wannan ya sanya masu mulkin mallaka suka hadu da babbar barazana. Da kuma
gazawar tunanin siyasa na kasashen yammacin duniya, sannan da gazawar akidun
kasashen yamma wadannan da suke ganin ta wannan hanyar ne kawai al'umma zata
iya cin nasara. Farkawar musulunci ta samu kafuwa acikin zukatan al'ummar
musulmi, sannan da gazawar masu mulkin mallaka wadda ta faru a wurare masu yawa
wajen gamawa da wannan halitta da take cikin zukatan al'ummar musulmi ta son musulunci,
wannan ya rayar da zukatan al'ummar musulmi.
Idan aka kalli Palasdin a yau wanda gwamnati
wadda ta tsayu akan kwaton yancin Palasdin, idan muka kwatanta da rishin galihu
da halin kaka na ka yi da alu'ummar palasdin suka kasance aciki, sannan idan
aka kalli Lebanon inda musulmi suka bayar da rayuwar ta yadda suka fuskanci
kasar Isra'il wadda ta mallaki manmanyan makamai tare da taimakon Kasar Amurka
da kasashen Turai, suka iya karya wannan kasa tare taimakon Allah, idan aka
kwatanta Lebanon a lokacin da Isra'il duk lokacin da suke so ba tare da wata
wata ba, zasu iya yin duk abin da sukeso.
Idan muka kalli Irak wadda mutanenta masu
kishi suka buwayi Amurka, sojoji da 'yan siyasar Amurkja wadan da suke hura
hanci akan mallaka kasar Irak, a yau suna cike da fuskantar matsaloli
daban-daban da suka shafi soja da tattalin arziki, idan kwatanta wannan Irak da Irak a lokacin
Azzalumin shugabanta wanda ya kasance yana
shan jinin bayin Allah.
Idan muka kalli Afganistan wadda dukkan
alkawullan Amurka da kasashen Turai suka kasance karya da yaudara, sannan suka
kai hari tare da sojojin kawance wanda yana da wahala a sami kamarsa a tarihin kasashen
yamma, bayan ruguza kasar Afganistan da haifar da talauci ta kissan al'umma a
wannan kasa, da karfafa kungiyoyin boye masu samar da muyagun abubuwan sanya
maye, babu wani alheri data samar wa wannan kasa ta Afganistan.
Daga karshe tare da la'akari da kasantuwar
kasashen musulmi da cigaban da yake acikin kasahsen musulmi da karkata ga
addini da kihsin musulunci, da kin Amurka da kasashen turai, wani abu ne wanda
za a yi alfahri da shi..
Tare da la'akari da dukkan abin da muka yi
bayani a sama, zamu iya tsinkayo
gushewar siyasa marar cin nasara ta kasashen yamma da samar da hadin kai
tsakani al'ummar muslmi da samara da duniyar muslunci mai karfi.
A halin yanzu Amurka da kasagshen Yamma da
mabarnatan shugabannin haramtacciyar kasar Isra'il sun fahimci hakikanin
farkawar al'ummar musulmi, sannan sun tabbatar da rashin amfanin karfin soja
wajen fuskantar al'ummar muslmin, don haka ne suke bin hanyoyi daban-daban na siya
da dubaru don cimma mummunan gurinsu.
Daya daga cikin hanyoyin da suke bi na dubaru
a yau wajen cimma wannan guri nasu, shi ne haifar da sabani a cikin al'ummar
musulmi, ta hanyoyi daban-daban wadanda suka hada da amfani da kudi da duk wata
hanya wadda zata kai su ga gurinsu ta hanyar samar da sabani tsakanin musulmi
ta yadda zasu dauke hankali musulmi ta hanyar sanya su rigima da junansu. Ta
yadda zasu sake hada rigima da junanmu wadda zai iya kai ga kashe-kashe a
tsakanin juna.
A yau duk wani motsi na haifar da sabani a
tsakanin musulmi wani zunubi ne wanda
yake komawa ga tarihi. Wadanda da gangan suke kafirta dinbin al'ummar musulmi,
ta hanyar fakewa da wasu dalilai marasa tushe, wadanda suke aibanta akidun
sauran al'ummar muslmi ta hanyar zato marar tusha, wadanda suke aibanta kwazon
matasa musulmin Lebanon wadanda suke kasance abiin alfahri ga al'ummar musulmi,
w3adanda suke aikin don faranta wa Amurka da gwamnatin sahayina, suna yin Magana
akan wani hadari wanda suka kirkira da kansu wai shi mai suna (jaririrn watan
shi'a) Abin da ake nufi da shi(wai wani hadari ne wanda zai faru ta hanyar
samar da kashen Shi'a wadan suka hada Iran, Irak, Siriya, da Lebanon) wadanda
suke aiki don durkusar da kasar musulmin
Irak, sannan su haifar da kashe juna da kawar da kwanciyar hankali a Irak,
wadanda suke takura zababbiyar gwamnatin Palasdin,, ta kowace hanya. Ko sun
sani ko ba su sani ba suna matsayin masu tafka mummunan laifi, sannan tarihin
musulunci da al'ummar musulmi na nan gaba zasu yi Allah-wadai da wannan aiki
nasu, sanann zai dauke su a masatyin 'yankoren makiya.
Al'ummar musulmi na duniya baki daya su
sani cewa, lokacin tozarta musulunci da mayar da musulmi koma baya ya riga ya wuce, sannan an riga an shi ga sabon
yanayi. Sannan wanna mummunan tunani wanda yake nuna cewa kasashen musulmi dole
ne su cigaba da kasamcewa a karkashin mulkin mallakar kasashen yamma wanda ya
hada da siyasa da al'adu, sannan abinda ya shafi tunani da aikin dai-daiku da
na al'umma dole ne ya kasance suna koyi ne da kasashen yamma, wannan ya riga ya
kau acikin zukatan al'ummar musulmi, kuma wannan ya faru ne ta hanyar zalunci
da jiji da kan kasashen yammacin duniya, ta yadda musulmi suka farka suka
fahimci makircinsu.
Kasashen yamma mussamman bayan kasantuwar
Amurka a matsayin shugaba, ta hanyar zalunci a bayyane ayyuka da mu'amalar da
ta saba wa hankali, da girmankai da jiji da kai marar iyaka na kasashen yamma,
ya sanya kashen musulmi sun dauki wadannan kashen a matsayin masu yaki da addininsu. Aikinsu dangane da
Palasdin da kuma yadda suke mu'amala da haramtacciyar kasar Isra'il, sannar da
matakan da suke dauka dangane da makaman kare dangi wanda kasar isra'il ta
mallaka, sannan da matakain da suke dauka dangane da shirin makamashin nukiliya
wnada bai shafi makami ba a iran, sannan da goyon bayan da suka nuna wa Isra'il
wajen kai wa Lebanon hari, ta hanyar taimakon Isra'il da makamai da hanyoyin
siyasa, sannan da nuna rashin goyon bayansu akan Kare kan da al'ummar Lebanon
suke yi wa kansu daga kasar Isra'il, Sannan da tatsar da suke yi a koda yaushe akan kasashen larabawa
da bayar da taimakonsu ga kasar Isra'il, da nuna goyon bayansu ga masu tozarta
addinin musulmunci, kai harda tozarcin wasu manya daga cikin shugabannnin yamma
wadanda suka hada da (pop) shugaban kiristocin katolika akan addinin musulunci,
sannan da daukar wanda ya yi bincike akan abin da ya shafi holokos da akidun
yahudawan sahayina, a matsayin mai laifi, sannan kai hari da kasha dimbin
al'ummar musulmi a Irak da sunan dimokradiyya, da ruguza gydaje da rayuwar
al'ummar iraki duk da suna dimokradiyya, sannan fito na fito da da gwamnatin da
al'umma suka zaba ta Palasdin, Irak, Da sauran kasashen Amurka ta kudu, da duk
gwamnatocin da 'yan koren Amurka da kasashen yamma ba su su ke mulki ba.
Guguwar yaki da ta'addanci, ta bangare guda kuma suna tattaunawa da bayar da
taimako da kungiyoyin ta'addanci a Irak da sauran wurare.
Irin
wadannan ayyuka da suka saba wa hankali sun zama hujja ga al'ummar musulmi,
sannan sun taimaka wajen farkar da al'ummar musulmi. A yau ko suna so ko ba su
wani motsi mai karfi ya riga
ya kunno kai a duniyar muslmi, sannan wannan motsin ne a lokacin da ya dace zai
dawo da izza da mutunci al'ummar musulmi.
Wannan
lokaci yana matsayin mai karfafa
hakan, don haka masana da malamai suna da wani muhimmin nauyi da ya hau kansu.
Saboda haka duk wani saku saku da nuna halin ko in kula zai iya janyo babbar asara ga al'ummar
musulmi. Malaman addini bai kamata ba su yi shiru dangane da raba kan al'ummar musumi,
hakanan masana kada su yi wata-wata wajen fadakar da matasa akan halin da
al'ummar musulmi suke acikin, da kaucewa wannan tarko na makiya musulunci. Yan
siyasa da shugabanni ya kamata su rike al'ummar su a wannan fage na fadakarwa,
sannan su dogara da al'ummarsu, gwantocin musulmi ya kamata su kara samura da
hadin kai a tsakaninsu, ta yadda zasu yi amfani da wannan karfi da suke da shi
na hakika wajen yakar mulkin mallaka na kashaen yamma.
A yau kungiyoyin leken asirin na Amurka da
Emgila a iraki, Lebanon,
da wasu daga cikin kasashen Arewacin
Afrika suna iya kokarinsu ta yadda zasu ga cewa sun samar da sabanin akida
acikin al'ummar musulmi. Taron hajji ya kamata ya zama wani riga kafi ko magani
akan wannan mummunan cuta da take bibiyarmu, Ayar nan da take cewa :"Ku bi
Allah ku bi manzonsa, kuma kada ku yi jayayya a tsakaninku, sakamakon haka
mutumcinku zai kau, kuma ku yi hakuri lallai Allah yana tare da masu
hakuri".ya kamata ko yaushe ta kasance a gabanmu.
A yau bara'a ga mushrikai wani kira ne wanda
a cikin zukatan al'ummar musulmi.sannan taron aikin hajji wani taro ne wanda
zai iya tabbatar da wannan kira wannda yake kunshe acikin halittar bil Adama.
Ya kamata ku yi amfani da wannan dama, ku yi
addu'a ga dukkan musulmi da yin addu'a don bayyanar Imam mahdi a.s. wanda zai
yantar da al'ummar muslmi daga wannan bakin zaunci da suke cikinsa, sannan ku
yi iya kokarinku don ku wanke kawunanku
acikin wannan teku.
Ina rokon Allah da ya sanya ku dace acikin
rayuwa ya kuma amsa maku hajjinku.
Sayyid Ali Khamna'i
3-12-1427